Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bada labari game da maganin abinda ke taso da tambayoyin da Shaidan yake sa wasiwasi akan su ga mumini. Sai Shaidan ya ce: Waye ya halicci abu kaza? waye ya halicci kaza? waye ya halicci sama? kuma waye ya halicci kasa? Sai mumini ya ba shi amsa a Addinance da dabi'ance da hankalce da fadinsa: Allah ne. Saidai Shaidan ba ya tsayawa a wannan iyakar na wasiwasi, kai yana cirata har sai ya ce: Waye ya halicci Ubangijinka? A wannan yayin ne mumini zai ture wadannan wasiwasin da al'amaura uku: Da yin imani da Allah. Da neman tsarin Allah daga Shaidan. Da kuma tsayawa kada ya zarce akan wasuwasin.