explain-icon

Bayani

Wani mutum ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, lallai cewa ni hakika na aikata dukkanin zunubai da sabo, ban bar wani karamin laifi ba ko babba sai da na aikata shi , shin za'a gafarta mini? Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa: Shin baka shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah ba ?? kuma Muhammad Manzon Allah ne? Ya maimaita masa sau uku. Sai ya amsa masa: Eh ina shaidawa, Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata gare shi - ya ba shi labarin falalar shahada biyu, da kuma kankarewarta ga munanan laifuka, kuma lallai cewa tuba yana kankare abinda ke kafinsa.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Girman (Kalmar) shahada biyu da kuma rinjayarta akan zunubai ga wanda ya fadeta yana mai gaskiya daga zuciyarsa.
  • Musulunci yana kankare abinda ke kafinsa.
  • Tuba na gaskiya yana shafe abinda ke kafinsa.
  • Maimaitawa a cikin ilimantarwa yana daga shiryarwar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
  • Falalar (Kalmar) shahada biyu, kuma cewa su sababi ne na tsira daga dawwama a cikin wuta.