explain-icon

Bayani

Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bayyana cewa abinda musulmi yake samu na cutuka da bakin cki da takaici da masibu da tsanani da tsoro da yunwa - kai koda akwai kayar da za ta taba shi ta sashi radadi -, hakan zai zama kaffara ga zunubansa da kuma kankare kurakuransa.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Bayanin falalar Allah ga bayinSa muminai da kuma rahamarSa garesu ta hanyar gafarta zunubai da mafi karancin cutar da zata samesu.
  • Ya kamata ga musulmi ya nemi ladan abinda ya sameshi a wurin Allah, ya kuma yi hakuri akan dukkanin karami da babba, dan ya zama yana samun daukakar darajoji da kuma kankarewa ga munanan laifuka.