explain-icon

Bayani

Wani mutum ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbat agare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, lallai dayanmu yana jin wani al'amari yana bijiro masa a zuciyarsa, saidai ya fade shi abu ne mai girma ne wanda ya kai matakin ace ya zama toka ya fi soyuwa agare shi akan ya fadeta. Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi kabbara sau biyu ya godewa Allah da ya mayar da kaidin Shaidan zuwa ga mujarradin wasuwasi.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Bayanin cewa Shaidan yana dakon muminai da wasuwasi; dan ya juyar da su daga imani zuwa kafirci.
  • Bayanin raunin Shaidan game da ma'abota imani yayin da bai samu wani iko ba sai wasiwasi kawai.
  • Yana kamata ga mumini ya bijirewa wasiwasin Shaidan da kuma tunkude shi.
  • Halaccin kabbara yayin wani abu abin so ko mamaki, daga gareshi ko mai kama da shi daga al'amaura.
  • Halaccin tambayar musulmi ga malami game da dukkanin abinda yake rikitar da shi.