Faɗima - Allah Ya yarda da ita - 'yar manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - takai koken abinda take fama dashi na gurbin kayan niƙan da take niƙawa, lokacin da ribatattu suka zo wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ta tafi zuwa gare shi zata tambaye shi ɗan aiki daga waɗannan ribatattun; dan ya tsaya a matsayinta akan ayyukan gida, sai dai cewa bata sameshi a gidansa ba, sai ta samu A'isha - Allah Ya yarda da ita -, sai ta bata labarin hakan, Lokacin da tsira da amincin Allah su tabbata agare shi dawo sai Nana A'isha ta ba shi labarin zuwan Faɗima wurin shi dan ta tambaye shi ɗan aiki ne, sai Annbi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo wurin Nana Faɗima da Aliyu - Allah Ya yarda da su - a gidansu alhali su suna kan shinfiɗa suna shirin barci, sai ya zauna tskaninsu har Aliyu - Allah Ya yarda da shi - ya ji sanyin diga-digan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - akan cikinsa, sai ya ce: Shin bana sanar daku mafi alheri daga abinda kuka tanbayeni ba akan na baku ɗan aiki? Suka ce: Eh, sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Idan kun kwanta dan yin bacci da daddare, to ku yi kabbara sau talatin da huɗu, da faɗin: Allahu Akbar, ku yi tasbihi sau talatin da uku, da faɗin: Subhanallahi, ku yi hamdala sau talatin da uku, da faɗin: Alhamdulillah; to wannan zikirin shi ne mafi alheri gareku daga ɗan aiki.