Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi yana ba da labarin cewa wanda Allah Ya nufe shi da alheri, to, sai ya azurta shi da fahimta a addininSa tsarki ya tabbata a gare shi. Kuma shi [Annabi] tsira da aminci su tabbata a agare shi Mai rabawa ne, yana raba abin da Allah Ya ba shi na arziki da ilimi da wanin haka, Kuma hakikanin wanda yake bayarwar shi ne Allah, amma duk wanda ba shi ba, to, su sabubba ne, ba sa anfanarwa sai da izinin Allah, Kuma lalle wannan al’ummar ba za ta gushe a kan al’amarin Allah ba, wanda ya saɓa musu ba zai taba cutar da su ba , har ƙiyama ta tashi.