Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bayyanawa acikin Hadisi Kudsi cewa Allah - Mai girma da daukaka - Ya sanar game da mushrikai da kafirai cewa su suna karyataShi suna siffantaShi da tawaya da aibobi, kuma hakan bai kamacesu ba. Amma karyatawar da suka yi wa Allah: Ita ce riyawarsu cewa Allah Ba zai dawo da su bayan mutuwarsu ba akaro na gaba, kamar yadda Ya haliccesu tun afarko da ba su, sai ya yi musu raddi da cewa Wanda Ya fari halitta daga babu mai iko ne akan dawo dasu kai hakan mafi sauki ne ma, duk da al'amarin dangane da Allah daidai ne halitta da dawowa, Allah Mai iko ne akan dukkan komai. Amma aibantawar: To fadinsu: Cewa Shi Yana da Da, sai ya yi musu raddi da cewa Shi ne daya Kwal, Mai kadaituwa da dukkanin cika a sunayenSa da siffofinSa da ayyukanSa, abin tsarkakewa daga kowacce tawaya da aibi, abin nufi da bukata wanda baYa bukatuwa ga wani, kuma kowa mai bukatuwane gareShi, kuma bai zama mahaifi ga wani ba, kuma baShi da wani Da, kuma baShi da tamka, tsarki ya tabbatar maSa Ya daukaka.