Daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - da isnadi: "Lokacin da Allah ya halicci halitta, ya rubuta a cikin wani littafi, kuma yana tare da shi a kan karaga: Rahamata ta rinjayi fushina." Kuma a cikin littafin: "Ta shawo kan fushina," kuma a cikin littafin: "Na riga fushina." Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi