Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bamu labarin cewa wanda ya furta kalmar tauhidi yana masanin ma'anarta yana mai aiki da abinda ta hukunta, ya kuma shaida da ubudiyyar Annabi Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da kuma manzancinsa, ya kuma yarda da kasantuwar Annabi Isa bawa ne na Allah da kuma manzancinsa, kuma cewa Allah Ya halicce shi da fadinSa "Ka sance" sai ya kasance , kuma cewa shi ruhi ne daga rayukan Allah wadanda Allah Ya haliccesu, ya kuma barrantar da babarsa daga abinda yahudawa suke jingina mata, ya yi imani da cewa aljanna gaskiya ce, kuma wuta gaskiya ce, yana mai kudirce samuwarsu, kuma cewa su ni'imar Allah ne da azabarSa, kuma ya mutu a kan hakan, to makomarsa tana aljanna koda ya kasance ya gajiya ne a ayyukan da'a, kuma yana da zunubai.