Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bada labarin cewa idan 'yan aljanna suka shiga aljanna, Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - zai ce musu: Shin kuna son wani abu da zan ƙaro muku? Sai 'yan aljanna gaba ɗayansu su ce: Shin baKa hasakaka fuskokinmu ba? Shin baKa shigar da mu aljanna ba, kuma Ka tseratar damu daga wuta? Sai Allah Ya gusar da shamaki kuma Ya ɗauke shi; hijabinSa (shi ne) haske, ba'a basu wani abuba mafi soyuwa garesu daga duba zuwa Ubangijinsu - Mai girma da ɗaukaka ba.