Abu Musa al’Ash'ari - Allah Ya yarda da shi - yana bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya aike shi Yaman, sai ya tambaye shi game da wasu kayan shaye-shaye waɗanda ake yin su a can, shin su haramun ne, sai ya tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da su. Sai Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Shi ne Bit'u: Tsimin zuma, da Mirzu: Tsimin shinkafa. Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce alhali ya kasance haƙiƙa an ba shi matattaran kalmomi: «Duk abin da yake sa maye haramun ne».