Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa idan aka ajiye jana'aiza (gawa) akan gado (makara), maza suka ɗauketa akan wuyansu, idan ta kasance ta gari ce zata ce: Ku gabato da ni dan abinda ta gan shi a gabanta na ni'ima, idan ba tagari ba ce zata yi ƙara da sauti abin ƙi: Ya halakarta ina zasu tafi da ita?! dan abinta ta gan shi a gabanta na azaba, kowane abu yana jin sautinta sai mutum kawai, da a ce ya ji shi da ya suma saboda tsananin abinda ya jishi.