Daga Bara'u ɗan Azib - Allah Ya yarda da shi - manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan aka tambayi musulmi a cikin ƙabari: Yana shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (Annabi) Muhammad manzon Allah ne". to wannan shi ne faɗinSa: {Allah Yana tabbatar wa waɗanda suka yi imani da faɗa tabbatacciya a cikin rayuwar duniya da kuma lahira} [Ibrahim: 27]. Ingantacce ne - Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi
explain-icon

Bayani

Za'a tambayi mumini a cikin ƙabari, sai mala'iku biyu waɗanda aka wakilta da hakan su tambaye shi su ne Munkar da Nakir, kamar yadda ambatansu ya zo a Hadisai masu yawa, sai ya shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah , kuma cewa (Annabi) Muhammad manzon Allah ne, Annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: wannan shi ne tabbatacciyar magana wacce Allah Ya faɗa a cikinta: {Allah Yana tabbatar da wadanda su ka yi imani da magana matabbaciya a rayuwar duniya da kuma a lahira} [Ibrahim: 27].

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Lallai cewa tambayar ƙabari gaskiya ne.
  • Falalar Allah ga bayinSa muminai a duniya da lahira ta hanyar tabbatar da su akan tabbatacciyar magana.
  • Falalar shaidawa da Tauhidi da mutuwa akan hakan.
  • Tabbatar war Allah ga mumini a duniya da tabbata akan imani, da shiga hanya madaidaiciya, a lokacin mutuwa kuma da mutuwa akan Tauhidi, a ƙabari a lokacin tambayar mala'iku biyu.