Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shiga dakinsa ga A'isha - Allah Ya yarda da ita - sai ya sameta ta rufe jarkarta karama wacce take sanya kayanta a ciki da wani yanki a jikinsa akwai hotunan masu rayuka, sai launin fuskarsa ya canja dan fushi saboda Allah sai ya cire shi, ya ce: Mafi tsananin azaba a ranar Alkiyama wadanda suke kamanta halittar Allah da hotunansu. A'isha ta ce: sai muka maida shi shinfida ko shinfidu biyu.