Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - yana bayyana cewa surorin Alkur’ani sun kasance suna sauka ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - amma ba ya sanin rabewarsu da karewarsu har sai {Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai} ta sauka gareshi, sai ya san cewa surar da ta gabata an cikata, kuma cewa ita farko ce ga sabuwar sura.