Nana A'isha uwar muminai - Allah Ya yarda da ita - ta bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya lazimci i'itikafi a goman ƙarshe na Ramadan, dan neman Lailatul Qadr, kuma ya zarce akan hakan har zuwa lokacin da Allah Ya ɗauki ransa, haƙiƙa matansa - Allah Ya yarda da su - sun lazimci i'itikafi a bayansa.