explain-icon

Bayani

Wani mutum daga sahabbai ya ce: Ina ma na yi sallah in huta, kai ka ce waɗanda ke gefensa sun aibata hakan gare shi , sai ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa: Ya kai Bilal! ka kira sallah ka yi iƙamarta; don mu samu hutu da ita; saboda abin da ke cikinta na ganawa da Allah - Maɗaukakin sarki - da kuma hutu ga rai da zuciya.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Hutun zuciya yana kasancewa ne da yin sallah; saboda abin da ke cikinta na ganawa da Allah - Maɗaukakin sarki -.
  • Inkari a kan wanda ya ke yin nauyin (jiki) game da ibada.
  • Wanda ya ba da wajibin da yake a kansa, ya kuɓutar da wuyayensa daga shi, hutu zai tabbata ta hakan gare shi da samun nutsuwa.