explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bamu labarin cewa wanda ya karkatar da wani abu daga abinda yake wajaba ya zama na Allah ne zuwa waninSa, kamar rokon wanin Allah - Madaukakin sarki - ko neman agaji ga waninSa, ya kuma mutu akan hakan to cewa shi yana daga 'yan wuta. Dan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya kara cewa wanda ya mutu alhali ba ya hada wani abu da Allah to makomarsa tana aljanna.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Addu'a ibada ce ba'a yinta sai ga Allah - Madaukakin sarki -.
  • Falalar tauhidi, kuma cewa wanda ya mutu akansa zai shiga aljanna, koda an yi masa azaba akan sashin zunubai.
  • Hadarin shirka, kuma cewa wanda ya mutu akanta zai shiga wuta.