Annabi-Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi yana bamu labari acikin wannan Hadisi cewa Mumini wani lokaci wani abu na masibu yakan same shi akansa ko Dukiyarsa ko waninsa, kuma cewa Allah zai bashi lada akan kowace Musiba ce ta Sameshi, Sannan ya bayyana cewa Musibu koyaushe suka zamo Manya kuma hadarin su ya girmama to ladansu yakan girmama a wajen Allah Sannan Annabi yayi bayanin cewa cewa afkuwar Musibu yana daga cikin Alamomin Son Allah ga Mumini, Kuma Hukunin Allah da Kaddararsa babu Makawa sai sun afku, sai dai kuma wanda yayi Hakuri kuma ya yarda da Kaddarar , to Allah zai saka masa kan hakan da Yardarsa kuma babu ladan da yafi wannan, kuma duk wanda ya yayi fushi kuma yaki yarda da Kaddarar Allah to Allah zai fushi da shi , kuma babu ukubar da tafi wannan.