Uƙbah ɗan Amir - Allah Ya yarda da shi - ya bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa: A daren nan Allah Ya saukar min da wasu ayoyi ba'a taɓa ganin kwatankwacinsu ba - wato a neman tsari (Dafa'i) - sune A'uzai guda biyu: Surar {Ƙul A'uzau bi rabbil falaƙ}, da surar {Ƙul A'uzu bi rabbin Nas}.