Daga Abu Sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi -: Cewa wani mutum ya ji wani mutum yana karanta: {Ka ce Shi ne Allah Shi kaɗai}, yana maimaita ta, lokacin da ya wayi gari sai ya zo wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya fada masa hakan, kai ka ce mutumin yana ganin ƙanƙantarta, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake hannunSa, lallai cewa ita ta yi daidai da ɗaya bisa uku na Alƙur'ani". Ingantacce ne - Bukhari ne ya rawaito shi
explain-icon

Bayani

Abu Sa'id al-Khudr - Allah Ya yarda da shi - ya fadi cewa wani mutum ya ji wani mutumin daban yana karanta Suratu (Ikhlas): {Ka ce Shi ne Allah Shi kaɗai} yana maimaitata a kowanne dare ba ya ƙari akanta, lokacin da ya wayi gari sai ya zo gurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ambata masa haka, kamar shi mai maganar yana ganin cewa ta yi kaɗan, sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi rantsuwa akan ma'anar ƙarfafawa: Na rantse da wanda raina yake a hannunSa lallai cewa ita (Surar) ta yi daidai da ɗaya bisa uku na Alƙur'ani.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Falalar Suratul Ikhlas, kuma ita tana daidai da ɗaya bisa uku na Alƙur'ani.
  • Halaccin karatu a sallar tsayuwar dare koda da ayoyi kaɗan ne da kuma maimaita su, da rashin ƙaranta hakan.
  • AlMaziri ya ce: An ce: Ma'anarsa: Cewa Alƙur'ani yana da ɓangarori uku; Kissoshi da hukunce-hukunce da kuma siffofin Allah - Maɗaukakin sarki -, {Ka ce Shi ne Allah Makaɗaici} mai tacewa ce - yana nufin ga siffofin Allah -, dan haka ita ce ɗaya bisa uku, kuma wani yanki daga cikin yankuna uku. Kum an ce: Ma'narsa: Cewa ladan karantata ana ninka shi da gwargwadan ladan karatun ɗaya bisa uku na Alƙur'ani ba tare da ninkawa ba.