Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi gargaɗi daga sakaci a aikata ƙananan zunubai, da kuma yawaitasu domin cewa su idan sun taru zasu halakar, kuma ya buga misali akan hakan da wasu mutanen da suka sauka a cikin wani kwari, sai kowanne daga cikinsu ya zo da ita ce ƙarami, har sai da suka sa gurasarsu ta nuna saboda taruwar abinda suka tara na itatuwan, kuma lallai ƙananan zunubai a duk lokacin da aka kama mai aikatasu da su bai tuba daga garesu ba ko kuma Allah bai yi masa afuwa ba to zasu halaka shi.