Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa akwai wani mutum daga waɗanda ke gabaninku ya kasance rauni ya same shi, sai ya kasa haƙuri bai yi haƙuri akan raɗaɗin ba, sai ya ɗauki wuƙa sai ya yanke hannunsa da ita kuma ya gaggautowa mutuwa, jinin bai tsaya ba har ya mutu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Bawa Na ya yi miNi gaggawa da ransa, haƙiƙa na haramta masa aljanna.