Wasu mutane biyu sun zo wajen Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a Hajjin ban kwana, alhali shi yana raba sadaka (zakka), kuma suka nemi ya basu daga cikin zakkar, sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya sake kallonsu, dan ya gane halinsu, kuma shin ya halatta a basu sadakar ko a'a? Sai ya gansu mazaje ne biyu ƙarfafa, sai ya ce: Idan kuna so zan baku daga cikin zakkar, babu rabo a cikinta ga wanda yake da dukiyar da zata ishe shi, ko ga wanda yake da ikon yin aiki ko juya dukiya, ko da ba shi da dukiyar da za'a ɗauke shi (a matsayin) mawadaci da ita.