Umar - Allah Ya yarda da shi - ya bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ga wani mutum ya gama alwalarsa, sai ya bar gwargwadan farce a ƙafarsa (Lam’a) ruwa bai same shi ba, sai ya ce masa yana mai nuni zuwa gurin da bai sami ruwa ba: Ka koma ka kyautata alwalarka ka cikata ka ba wa kowacce gaba haƙƙinta na ruwa. Sai mutumin ya koma ya cika alwalarsa, sannan ya yi sallah.