Uwar muminai Ummu Salama - Allah Ya yarda da ita - ta ambaci cewa ita ta ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa wata rana: Babu wani musulmin da wata musiba zata same shi sai ya faɗi abinda Allah Ya so gare shi: {Lallai mu daga Allah muke kuma lallai mu zuwa ga Allah zamu koma} [al-Baƙara: 156], (Ya Allah Ka bani lada) Ka bani ladan haƙurina (a cikin wannan musiba), ka canja mini (Ka maye mini gurbi) daga ita (da mafi alheri daga gareta); sai Allah Ya canja masa mafi alheri daga gareta. Ta ce : Lokacin da Abu Salama ya yasu na ce: Waye cikin musulmai ya fi Abu Salama alheri?! farkon gidan da ya yi hijira zuwa ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sannan Allah Ya taimake ni sai na faɗeta, sai Allah Ya maye mini gurbin Abu Salama da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbta agare shi -.