Daga Abu Sa'id AlKhudri - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - Zai cewa 'yan aljanna: Yaku 'yan aljanna? sai su ce: AmsawarKa ya Ubangijinmu da dai amsawarKa, sai Ya ce: Shin kun yarda? Sai su ce: Dan me ba zamu yarda ba alhali Ka bamu abinda baKa bawa wani daga halittarKa ba? Sai Ya ce: Ni zan baku mafifici daga hakan, sai su ce: Ya Ubangiji, wane abu ne maffifici daga hakan? Sai Ya ce: Zan saukar muku da yardata, ba zan yi fushi daku ba a bayansa har abada". Ingantacce ne - Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi
explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa Allah - Maɗaukakin sarki - zai cewa 'yan aljanna alhali su suna cikinta: Yaku 'yan aljanna, sai su amsa maSa suna masu cewa: AmsawarKa ya Ubangijinmu da dai amsawarKa, Sai Ya ce musu: Shin kun yarda? sai su ce: Eh mun yarda; Danme ba zamu yardaba alhali ka bamu abinda baKa bawa wani daga halittarka ba! Tsarki ya tabbatar maSa Zaice: Shin ba zan baku mafifici daga hakan ba? Sai su ce: Wane abu ne mafifici daga hakan?! Sai ya ce: Zan saukar muku dawwamammiyar yarda ta; ba zan yi fushi daku a abayanta ba har abada.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Zancen Allah - Mai girma da ɗaukaka - tare da 'yan aljanna.
  • Albishir daga Allah ga 'yan aljanna da yardarSa garesu, da saukar da yardarSa garesu, da rashin fushinSa har abada.
  • Yardar duk wani ɗan aljanna da yanayin halinsa tare da saɓanin matsayinsu da banbancin darajojinsu; domin dukkaninsu sun amsa da lafazi ɗaya shi ne: "Ka bamu abinda baka bawa wani daga halittarka ba".