Nana Aisha Uwar muminai A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Ya isheka daga Safiyya - tana nufin Uwar muminai - Allah Ya yarda da ita - cewa daga cikin aibukanta na jiki ita gajera ce, sai ya ce: Haƙiƙa kin faɗi kalmar da da za'a cakuɗata da ruwan kogi da ta rinjaye shi ta canjashi ta kuma ɓata shi, ta ce: Kuma na aikata irin aikin wani mutum dan ɓata shi, sai Annabi - tsira da amincin Allsh su tabbata agare shi - ya ce: In ya faɗi aibinsa ba ya faranta mini rai, ko in kwaikwaye shi in aikata irin aikinsa ko in faɗi irin maganarsa ta fuskar tauyewa ko da kuwa an bani wani abu mai yawa na duniya akan haka.