Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya gargaɗar daga yin rantsuwa da Allah akan ƙarya kuma yana sane, hakan dan yankar haƙƙin wani mutum musulmi, domin cewa sakamkon hakan shi ne cancantar wuta, da haramta aljanna, kuma shi yana daga manyan zunubai. Sai wani mutum ya ce ya Manzon Allah: Koda abinda aka rantse akan shi ɗin wani abune dan kaɗan? Sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Koda hakan ya zama a itacen asuwakin da ake cira ne daga bishiyar ƙirya.