Daga Ubadah dan Samit - Allah Ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Babu sallah ga wanda bai karanta Fatiha ba".
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa sallah ba ta inganta sai da karanta suratul Fatiha, ita rukuni ce daga rukunan sallah a kowace raka'a.
Daga Cikin Fa idodin Hadisin
Wanin karatun Fatiha ba ya isarwa daga gareta tare da iko a kanta.
Bacin raka'ar da ba'a karanta Fatiha a cikinta ba, daga mai ganganci da jahili da mai mantuwa; Domin cewa ita rukuni ce, rukunai ba sa saraya ta kowanne hali.
Karatun Fatiha yana saraya daga mamu idan ya riski liman yana ruku'u.