Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa bawa idan ya mutu za'a bijiro masa da masaukinsa da gurinsa na musamman a cikin aljanna ko wuta, a farkon yini da ƙarshensa; wurinsa a aljanna idan ya kasance daga cikin 'yan aljanna, da kuma wurinsa a wuta idan ya kasance daga cikin 'yan wuta ne, kuma za’a ce masa: Wadannan wuraran ne wadanda za'a tasheka zuwa gare su ranar alƙiyama; a cikin hakan akwai ni'imtarwa ga mumini, da kuma azabtarwa ga kafiri.