Daga Zubair ɗan Awwam - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ɗayanku ya ɗauki igiyarsa, ya zo da curin itatuwa a gadan bayansa, ya saida su, Allah Ya kame fuskarsa da su, shi ne yafi alheri gare shi daga ya roƙi mutane sun ba shi ko sun hana shi». Ingantacce ne - Bukhari ne ya rawaito shi
explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa mutum ɗaya daga cikin mutane ya yi aiki kowane irin aiki ne koda zai ɗauki igiya ne, ya tattara itatuwa a gadan bayansa sai ya saida shi ya ci daga gare shi, ko ya yi sadaka da shi ya wadata daga mutane da shi kuma ya kare fuskarsa daga ƙasƙancin roƙo; shi ne ya fiye masa alheri daga ya tambayi mutane su ba shi ko su hanashi, roƙon mutane ƙasƙanci ne, mumini kuwa maɗaukaki ne ba ƙasƙantacce ba ne.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Kwaɗaitarwa akan kamewa daga roƙo da kuma tsarkaka daga gare shi.
  • Kwaɗaitarwa akan aiki dan samun arziƙi, koda an jarrabi baligi da ƙaramar sana'a wulaƙantacciya a idanuwan mutane.
  • Yaƙar da Musulunci yake yi wa roƙo; saboda haka ya wajabta yin aiki, ko da mai wahala ne; kamar saran ita ce misali.
  • Roƙo ba ya halatta tare da iko akan aiki da kuma neman arziƙi.
  • Roƙon sarki (shugaba) idan akwai buƙata ya halatta, Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: {Haka kuma babu (laifi) a kan waɗanda idan sun zo maka don ka basu abin hawa sai ka ce: "Bani da abin hawan da zan baku," sai suka juya idanuwansu suna kwararar da hawaye don baƙin cikin ba su sami abinda zasu ciyar ba}. [Al-Taubah: 92].
  • Wanda yake da larurar roƙo da kuma rauni akan neman kuɗi to ya halatta gare shi ya yi roƙo, amma kada ya yi naci, Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: {Basa nacin roƙon mutane} [Al-Baƙara: 273].
  • Nawawi ya ce: A cikinsa akwai: Kwaɗaitarwa akan sadaka, da kuma ci daga aikin hannunsa, da neman halal.