explain-icon

Bayani

Tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi ya kasance idan zai yi sujjada yana buɗa tsakanin hannayensa a tsakiyar sujjada; sai kowanne hannu ya nisanta daga gefan da yake biye masa, kwatankwacin fukafukai biyu, har launin fatar hammatarsa ya bayyana; wannan yana daga kai matuƙa a nisantar da zira'i biyu da kuma nisantar da su daga sasanninsu.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • An so wannan yanayin a cikin sujjada, shi ne nisantar da damatsansa biyu daga sasanninsa.
  • Mamun da na kusa da shi yake cutuwa da nisantarwar to ba'a shar’anta masa hakan ba.
  • Akwai hikimomi da fa'idoji masu yawa a cikin nisantar a cikin sujjada, daga cikinsu: Bayyanar da nishaɗi da kwaɗayi a cikin sallah, kuma idan ya dogara akan dukkan gaɓɓan sujjada sai kowacce gaɓa ta ɗauki haƙƙinta daga bauta. Akace: Hikima a cikin hakan ya yi kama da tawali'u, kuma mafi isuwa a cikin tabbatar da goshi da hanci a ƙasa, kuma dan banbance kowacce gaɓa da kanta.