Wani mutum ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, shin kana ganin idan wani mutum ya zo yana son ƙwatar dukiyata? Ya ce: Bai wajaba ka miƙa wuya ka ba shi dukiyarka ba, ya ce: Shin kana ganin idan ya yaƙeni? Ya ce: Yana halatta gareka ka yaƙe shi, ya ce: Shin kana ganin idan ya kasheni fa? Ya ce: To kai shahidi ne, ya ce: Shin kana ganin idan na kashe shi fa? Ya ce: Shi ya cancanci a yi masa uƙuba a cikin wuta a ranar alƙiyama.