Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa haƙiƙa ya rabauta wanda ya miƙa wuya ga Ubangijinsa sai aka shiryar da shi kuma aka datar da shi ga Musulunci, kuma aka azirta shi gwagwadan buƙatarsa daga halal ba tare da ƙari ko ragi ba, kuma Allah Ya sanya shi mai yarda da abinda Ya bashi.