Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fita daga wurin matarsa Uwar muminai Nana Juwairiyya - Allah Ya yarda da ita - a farkon yini lokacin da ya yi sallar Asuba, alhali ita tana zaune a wurin sallarta, sannan ya dawo bayan rana ta ɗaga lokacin sallar walaha, alhali ita ba ta gushe ba tana zaune a wurinta, sai ya ce: Shin baki gushe ba akan halin da na barki akansa? Ta ce: Eh, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Haƙiƙa a bayanki na faɗi wasu kalmomi huɗu, kuma na maimaita su sau uku, da za'a auna da abinda kika faɗa a gaba ɗayan lokacin da kike a zaune a cikinsa da sun rinjaye su: (Tsarki ya tabbata ga Allah) da tsarkakarSa daga dukkan tawaya, (da godiyarSa) inda Yake da kyakkyawan yabon da Ya shiryar ga hakan, (adadin halittarSa) waɗanda babu mai iya iyakancesu sai Allah, (da yardar kanSa) da gwargwadan abinda Ya yardar maSa ga wanda Allah Ya yarda da shi daga bayinSa kuma shi wani abu ne ba’a kewaye shi da sani , (da awon Al’arshin sa) wanda shi ne mafi girman halittu kuma mafi nauyinsu, (da tawadar kalmominSa) kuma kalmomin Allah ba sa taƙaituwa kuma ba sa ƙarewa; wannan yana gemawa kuma yana ƙunsar rabe-raben uku; domin tawadar kalmominSa - tsarki ya tabbatar maSa - babu karewa ga iyakarta, ko ga siffarSa ko ga adaddinsa, sai dai abin nufi: Kai matuka da shi a yawa; domin a farko ya ambaci abinda kirge mai yawa na adadin halitta yake iyakance shi , sannan ya hau zuwa abinda shi ne mafi girma daga nan kuma ya bayyanar daga gare shi da yardar kanSa, sannan awon mafi girman halittu shi ne al'Arshi; na farkon dan kirgawa ne da kuma yawa, na biyun kuma da siffa ne da kuma kaifiyya, na uku dan girma da kuma nauyi.