Daga Ummu Kais Bint Mihsan -Allah Ya yarda da ita -: Cewa ita ta zo da wani ɗanta ƙarami bai fara cin abinci ba zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zaunar da shi a ƙirjinsa, sai ya yi fitsari akan tufafinsa, sai ya sa a kawo masa ruwa, sai ya yayyafa ruwan bai wanke shi ba. Ingantacce ne - Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi
explain-icon

Bayani

Ummu Kais bintu Mihsan - Allah Ya yarda da shi - ta zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da wani ɗanta wanda bai fara cin abinci ba saboda ƙanƙantar shekarunsa, sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya zaunar da shi a ƙirjinsa, sai yaron ya yi fitsari akan tufafinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya sa a kawo masa ruwa, sai ya yayyafa ruwan akan tufafinsa bai wanke tufafin ba.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Kyawawan Ɗabi'un Annabi - tsira da amincin Allah su tabata agare shi - mai girma, da kuma tawali'unsa mai yawa.
  • An so kyautata kyakkyawar mu'amala da tawali'u da tausasawa ga ƙananan yara, da gyara zukatan manya ta hanyar girmama ƙananan yaransu da kuma zaunar da su a ƙirji, da makamancin haka.
  • Najasar fitsarin yaro ko da bai fara cin abinci daomin sha'awa ba.
  • Aikin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ana kiransa yayyafi, kuma ya keɓanci ƙaramin yaro ne wanda bai fara cin abinci ba, amma mace to babu makawa sai an wanke fitsarinta koda ta kasance ƙarama ce.
  • Bahayar yaro wanda yake cin abinci ta hanyar tsotson nonon mahaifiyarsa to babu makawa a cikin hakan sai an wanke kamar sauran najasa.
  • Babu makawa a wankewar daga wani al'amari na ƙari akan sanya ruwan.
  • Abin da ya fi yin gaggawa da tsaftace bigiren najasar; dan gaggawa a tsarkaka daga kabasin, kuma dan kada a manta.