A cikin wannan Hadisin cewa shi ya wajaba akan Musulmi Ji da kuma biyayya ga Shugabanni akan kowane hali, matukar dai basu yi Umarni da Sabo ba ko kuma sun dorawa Mutane abunda ba za'a iya ba, kuma koda akwai wuya cikin abunda suka dora din wani lokaci, kuma ko da wasu daga cikin hakkokinsu zasu rasa, saboda gabatar da Maslaha gamammiya akan Maslaha kebantacciya