Manzon Allah SAW yana tambayar Sahabbai amincin Allah a gare su sai ya ce: lp limsam wanda yafo kowa Talaucewa? sai suka basjo labarin abunda suka sani a Al-adance, sai suka ce: shi ne talakan bashi da ko sisi kuma bashi da Kadara, sai ya basu labarin cewa Matsiyaci a cikin wannan Al-ummar shi ne wanda yazo Ranar Alkiyama da kyawawan Ayyuka Manya, da kuma kyawawan Ayyuka Masu yawa na Sallah da Azumi da zakka sai ya zo amma ya Zagi wannan kuma ya daki wancan, kuma ya cinye kuxin wancan kuma ya jefi wancan ya zubar da jinin wancan, kuma ga Mutane suna son karbar haqqinsu, saboda abunda basu iya karvarsa a Duniya ba zasu karveshi a Lahira, sai a xaukar musu fansa sai a xauka daga ladan ayyukansa a bawa wannan ladansa kuma wannan ma a biyashi da ladansa da Adalci da kisasi na gaskiya, idan suka qare ayyukansa na Alkairin sai a xauki Zunubansu sai a lafta masa su, sannan a jefashi cikin Wuta