Aisha -Allah ya yarda da ita tana ambata mana cewa: Matan Sahabbai sun kasance suna lullube jikinsu da tufafinsu kuma su je sallar Asuba tare da Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi, kuma har su koma gidajensu ba mai gane su, duk da kasancewar haske ya dan fara bayyana, tare da sauran duhun. Littafin Taisiril Ahkam, na Malam Bassam, shafi na 86