Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya karanta
{قل يأيها الكافرون} da {قل هو الله أحد}
a raka'o'i biyu (kafin sallar) Asuba.
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana son a raka'o'i biyu na nafilar Asuba, a raka'a ta farko ya karanta surar
{قل يأيها الكافرون} [al-Kafirun].
A raka'a ta biyu kuma surar
{قل هو الله أحد} [al-Ikhlas].
Daga Cikin Fa idodin Hadisin
An so karanta waɗannan surori biyun bayan fatiha a sunnar (Raka’atal fajr) Asuba.
Waɗannan surori biyun ana ce musu Suratul Ikhlas; domin a cikin Suratul kafirun akwai kuɓuta daga dukkan abinda mushrikai suke bautawa koma bayan Allah, kuma su ba masu bautar Allah ba ne domin shirkarsu tana ɓata ayyukansu, kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Shi ne Mai wanda ya cancanci ibada, kuma cewa a cikin Suratul al-Ikhlas akwai kaɗaita Allah (da bauta) da kuma tsarkake (ibada) gare shi da bayanin siffofinSa.