Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annbai - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «‌Lallai cewa Allah idan Ya so wani bawa sai Ya kira Jibril sai Ya ce: Lallai cewa Ni ina son wane to ka so shi, ya ce: Sai Jibril yaso shi, sannan ya yi kira a cikin sama sai ya ce: Lallai Allah Ya na son wane to kuso shi, sai waɗanda ke sama su so shi, sannan a sanya masa karɓuwa a cikin ƙasa. Idan kuma Ya ƙi wani bawa sai Ya kira Jibril sai Ya ce; Lallai Ni ina ƙin wane to ka ƙi shi, ya ce sai (Mala’ika) Jibril ya ƙi shi, sannan sai ya yi kira a cikin waɗanda ke cikin sama lallai cewa Allah Yana ƙin wane to ku ƙishi, ya ce: Sai su ƙishi, sannan a sanya masa baƙin jini a cikin ƙasa». Ingantacce ne - Sahih Muslim
explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya labarta cewa Allah idan Ya so bawanSa mumini; mai biyayya ga umarninSa mai nisantar hane-hanenSa sai Ya kira (Mala’ika) Jibril: Lallai cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Yana son wane to ka so shi. Sai shugaban mala'iku (Mala’ika) Jibril - aminci ya tabbata agare shi - ya so shi, sai Jibril yayi kira a cikin mala'ikun sama: Lallai cewa Ubangijinku Yana son wane to ku so shi, sai waɗanda ke sama su so shi, sannan a sanya masa karɓuwa a cikin zukatan muminai da soyayya da kuma karkata gare shi da kuma yarda da shi. Idan Allah Ya ki wani bawanSa sai Ya kira Jibril: Lallai cewa Ni ina ƙin wane to ka ƙi shi, sai (Mala’ika) Jibril ya ƙishi, sannan Jibril yayi kira a cikin waɗanda ke cikin sama: Lallai Ubangijinku Yana ƙin wane to ku ƙishi; sai su ƙishi, sannan a sanya masa baƙin jini da ƙiyayya a cikin zukatan muminai.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Abu Muhammad Ibnu Abi Jamrah ya ce: A cikin gabatar da umarni da hakan ga (mala'ika) Jibril kafin waninsa cikin mala'iku akwai bayyanar da girman matsayinsa a wurin Allah - Maɗaukakin sarki - akan waninsa daga cikinsu.
  • Wanda Allah Ya so shi to halittun dake cikin sama da ƙasa zasu so shi, wanda Allah Ya ƙishi to halittun dake cikin sama da ƙasa zasu ƙishi.
  • Sindi ya ce: Faɗinsa (za'a sanya masa karɓuwa a cikin ƙasa), ba ya lazimtar gamewa, kai hakan akan gwargwadan abinda Allah Ya yi nufi ne na karɓuwa a doron ƙasa, ta yaya alhali ƙiyayyar mutanen banza ga zaɓaɓɓun mtane sananniya ce.
  • Kwaɗaitarwa akan cika ayyukan alheri akan saɓanin nau'ikansu farillansu da sunnoninsu, da kuma gargaɗarwa daga saɓo da kuma bidi'o'i; domin cewa su masu sabbaba zato ne na fushi.
  • Ibnu Hajar ya ce: Kuma ana fahimta daga gare shi cewa soyayyar zukatan mutane alamar soyayyar Allah ce, abinda ke cikin jana’iza yana ƙarfafa shi: "Kune shaidun Allah a doron ƙasa".
  • Ibnul Arabi al-Malaki ya ce: Kawai ana nufi da waɗanda ke cikin ƙasa wanda ya san shi daga cikinsu ne kawai banda wanda bai san shi ba, baima taɓa jinsa ba.