Daga Abu Yazid Al-ansari -Allah ya yarda da shi- ya ce: Manzon Allah SAW ya ce da ni: Manzon Allah SAW ya ce da ni: "Matso kusa da ni" sai na Matso kusa da shi, sai ya ce: "Ka shigar da Hannunka ka shafi bayana" ya ce: sai na shigar da Hannuna cikin Rigarsa, sai na shafi bayansa, sai yatsuna suka tava Hatimin Annabta, sai aka yambayeshi game da Hatimin Annabta sai ya ce: "Wani Gashi ne a tsakanin Kafaxunsa" Ingantacce ne - Ahmad ne ya rawaito shi