Daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya duba mara lafiya (wanda) ajalinsa bai yi ba, sai ya ce a wurinsa sau bakwai: Ina roƙon Allah Mai girma Ubangijin al-Arshi Mai girma Ya baka lafiya, sai Allah Ya ba shi lafiya daga wannan cutar". Ingantacce ne - Abu Daud ne ya ruwaito shi da Kuma Tirmizi da Ahmad
explain-icon

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa babu wani musulmin da zai ziyarci wani musulmi a cikin rashin lafiyarsa wanda lokacin mutuwarsa bai yi ba, sannan mai ziyarar ya yi wa mara lafiya addu'a da faɗinsa: (Ina roƙon Allah Mai girma) a cikin zatinSa da siffofinSa da ayyukanSa, (Ubangijin al-Arshi Mai girma Ya baka lafiya), kuma ya maimaitata hakan sau bakwai sai Allah Ya ba shi lafiya daga wannan cutar.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • An so addu'a ga mara lafiya da wannan addu'ar, da kuma maimaitata sau bakwai.
  • Tabbatar da waraka ga wanda aka faɗi wannan addu'ar a wurinsa da izinin Allah - Maɗaukakin sarki -, in ta bijiro da gaskiya da kuma salaha.
  • Zai faɗi wannan addu'ar ne a ɓoye da bayyane, dukkan hakan ya halatta, sai dai idan ya jiyar da mara lafiyar to shi ya fi; domin a cikinsa akwai shigar da farin ciki gare shi.