Annabi tsira da amincin Allah ya sauka a wani waje mai tudu kadan daga Makkah,sai Bilal ya fito ya yi alwala da sauran ruwan alwalar Annabi tsira da aminci su tabbata a gasre shi,sai mutane suka zo suna ta tabarruki da wannan ruwan alwala,sai Bilal ya yi kiran salla: sai Abu Juhaifa yace:sai na rika bibiyar bakin Bilal, yana jujjuya wa a dama da hargu yayin da ya zo"ku taso zuwa ga sallah,ku taso zuwa ga rabo: don mutane su ji,ko don su wadannan jumloli suna kwaditar da a zo sallah ne,sannan sai aka kafa wani dan gajeren mashi don ya zama sitirar sallarsa,sai ya sallaci azahar raka'a biyu,sannan bai gushe ba yana sallatar salla mai raka'a hudu bibbiyu har ya koma ko don kasancewarsa matafiyi