Daga Asim ya ce: na tambayi Anas -Allah ya yarda da shi- game da Al-qunuti, ya ce: kafin ya xago daga Ruku'u, sai na ce: lallai cewa Wane yana rayawa cewa kai kana cewa bayan ruku'u? sai ya ce: Yayi qarya, sannan ya gaya mana cewa Manzon Alllah SAW: "cewa shi yayi yayi al-qunuti wata xaya bayan Ruku'u, yana Addu'a ga wasu Mutane daga cikin Bani Sulaim" kuma ya ce: "Ya aika Mutum Arba'in ko Saba'in -yana dai kokwantn yawan- Na Makarantan Qur'ani zuwa ga wasu Mutane Mushirikai" sai waxan can Mutane suka far musu suka kashe su, kuma ya kasance a tsakaninsu akwai Manzon Allah SAW a lokacin "Ban tava ganin sa yayi bacin rai ba kamar bacin rai akan su" Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi