Wannan hadisin yana nuna tsoron ranar tashin kiyama da azabar wuta, kamar yadda Annabi –sallal Lahu alaihi wa alihi wa sallam - ya bayyana cewa daga cikin mutane ranar tashin kiyama akwai wadanda suka riski wutar su zuwa diddige, zuwa gwiwowinsa da kuma rikonsa, kuma wasu daga cikinsu sun kai wuyansa, saboda mutane sun sha bamban a cikin azaba gwargwadon ayyukansu a wannan duniya. Muna rokon Allah ya kara mana lafiya.