Manzon Allah -Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- cewa daga Alamar son Allah bawan sa da Alkairi yayi masa Magani da yi masa wata ukuba akan zunubansa a cikin Duniya har ya futa daga Duniya kuma babu komai akansa na zunubi da za'a kama shi da shi Ranar Alkiyama; domin cewa duk wanda akai masa Ukuba a Duniya ti Ukubarsa a Lahira zatayi Sauki, kuma yana daga cikin Alamomin nufin Sharri ga bawa a yi watsi da shi da Zunubansa a Duniya har yaje Ranar Al-kiyama da Tarin zunubansa har Allah ya yi masa sakamako da abunda ya cancance shi Ranar Alkiyama.