Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce: Manzon Allah ya ce: "Bawa da aka Mallaka Mai gyara yana da Lada Biyu"; saboda tsayuwa da hakkin Allah Madaukakin Sarki- na ibadu da tsayuwarsa da hakkin Maigidansa na Hidima, Sannan Abuhuraira -Allah ya yarda da shi- ya bada labarin cewa ba don babu Jahadi akan Bawa ba, da kuma tsayuwarsa ga Hidimar Mahaifiyarsa na ciyarwa da Hidima wallahi da na fi son in zamanto na Mutu a Matsayin yana Bawa sabida Ladan da yake cikinsa