explain-icon

Bayani

Sa'ad Ibnu Abi Waƙas - Allah Ya yarda da shi - ya bada labarin cewa shi ya kasance yana ganin farin kundukukin (kumatun) Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - saboda tsananin waiwayensa idan zai sallame daga sallarsa a damansa a sallamar farko, haka a hagunsa a (sallama) ta biyu.

explain-icon

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  • Halaccin kai matuƙa a cikin waiwaye zuwa ɓangaren dama da kuma ɓangaren hagu.
  • Halaccin sallama biyu zuwa dama da hagu.
  • Nawawi ya ce: Da a ce zai yi sallama biyu a damarsa ko a hagunsa ko ta ɓangaren fuskarsa, ko ta farkon a hagunsa, ta biyun kuma a damansa sallarsa ta inganta kuma sallama biyun ta tabbata, sai dai ya rasa falala ta yadda ake yinsu .