Sa'ad Ibnu Abi Waƙas - Allah Ya yarda da shi - ya bada labarin cewa shi ya kasance yana ganin farin kundukukin (kumatun) Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - saboda tsananin waiwayensa idan zai sallame daga sallarsa a damansa a sallamar farko, haka a hagunsa a (sallama) ta biyu.